Posts

Showing posts with the label Tarihin Sahabbai Mata

Tarihin Sahabbai Mata 3: Ummu Adiyya Al-Ansariyya

Image
UMMU ADIYYA AL-ANSARIYYA "Ta halacci yakoki bakwai tare da Manzon Allah" - Mausu’ at Hayatis-sahabiyyat Sunanta Nusaiba bnt Haris ( نسيبة بن حارث ), a wata fadar kuma bnt Ka’ab (بنت كعب ) . Amma Abu Amr ya musunta hakan yace Nusaiba bnt Ka’ab ( نسيبة بنت كعب ) ita ce Ummu Ammara ( أم عمارة ), amma ita wannan an fi saninta da Ummu Adiyya ( أم عادية الأنصارية ). - Al-Isabah 8/437 Ibn Sa ’ ad yace "Ummu Adiyya ta musulunta tun da wuri kuma ta halacci yakoki da masu yawa tare da manzon Allah. Kuma ta ruwaici hadisai masu yawa daga gareShi". - Dabakaat, 455 An ruwaito daga wajenta tana cewa " Na halacci yakoki bakwai (7) tare da Manzon Allah  ﷺ         mun kasance muna dafa musu abinci, kuma muna kula da abin hawansu tare da yin magani ga wadanda aka yi wa rauni muna kuma jinyarsu " - Mausu at Hayatis sahabiyyat Imamuz-Zahabiy yace " Ummu Adiyya tana cikin mafiya sani cikin sahabbai ta ruwaito hadisai masu yawa ...

Tarihin Sahabbai Mata 2: Ummu Rumana

Image
UMMU RUMANA AL-KINANIYAH ( أم رومان الكنانیة ) Sunanta Ummu Rumana bint Amir ibn Umaymir bn Abdulsham ibn Attab ibn Uzaifah ibn Subi'i bn Duhman ibn al-Haris ibn Ghanam ibn Malik ibn Kinana ( رضي الله عنھا و أرضاھا ). Ita ‘yace ga ‘Amir ibn Umaymir wanda su Banu Kinanahne. Sunan na asali shi ne Zainab kamar yadda aka ruwaito daga Ibn Ishaq. - Al’isaba 8/391 Ummu Rumana ta kasance mata gun Khalifan Manzon Allah ﷺ Abubakar as-Siddiq (R), kuma mahaifiya ga Nana A’isha da AbdurRahman bin Abubakar Assiddiq.  Ana mata kirari da cewa "Duk wanda yake son ya ga Hurul'ini tun a duniya to ya dubi Ummu Rumana" . - Tahzibul Kamal 35/259 A zamanin jahiliyya ta auri wani da ake kira Al-Haris bn Sakhbarah ( الحارث بن سخبرة ) ta Haifa masa al-Dufail. Bayan rasuwarsa sai ta auri Abubakar As-Siddiq (R). Ta musulunta tun da wuri ta mika wuya ga manzon Allah, sannan ta yi hijira zuwa Madina tare da Iyalan Gidan Manzon Allah ﷺ da 'ya'yanta da dukkan iyalan Ab...

Tarihin Sahabbai Mata 1: Maimunatu bint al-Harith (R)

Image
MAIMUNATU BINT AL-HARITH ( ميمونة بنت الحارث ) " Ita ce mata ta karshe a gidan Manzon Allah ﷺ " -   . Sunanta Maimuna ( ميمونة ) bint al-Haris ( الحارث ) bn Hazn ( الهزم ) Al-Hilaliyya ( الهلالية ), sunan mahaifiyarta Hind bint Awf ( هند بن عوف ) ‘yar qabilar Himyar ta Yemen. Maimunatu bint al-Harith ta kasance 'yar uwar Ummu Fadal ( أم فضل ). An haifeta a kafin Hijira da shekara 28 a garin. - Al-Isaba 8/192 Asalin sunanta Barratu ( برّة ) sai Manzon ﷺ Allah Ya canza mata suna zuwa Maimuna ( ميمونة ) ma’ana ‘ Mai albarka' . Kafin ta auri Manzon  Allah ﷺ ta auri Mas'ud bn Amr Athaqafy ( مسعود بن عمور الثقفى ) tun a lokacin Jahiliya (kafin zuwan Musulunci) sai suka rabu. Bayan nan sai ta auri Abu Ruhum bn Abdul Uzza ( أبو رهم بن عبدالعزى ) shi kuma rasuwa ( mut u wa ) yayi. Bayan rasuwarsa ne sai ta auri Manzon Allah ﷺ a lokacin da akayi Umarar Ramuwa ( عمرة القضاء ) a watan Dhul-Qa'adah shekara ta bakwai (7) bayan hijira a Sarif w...