Maganganun Malamai akan Mummunar Akidar Shia
MAGANGANUN MALAMAI AKAN MUMMUNAR AKIDAR SHI'AH GA KADAN DAGA CIKI NA FARKO: IMAM MALIK BN ANAS An ruwaitu daga Imam Malik yace: " Wanda yake zagin sahabban Manzon Allah bai da rabo ko kuma cewa ya yi bai da kaso a cikin Musulunci" Almajirin Imam Malik mai suna Ashhabu ya ce: An tambayi malik dangane da Rafilawa”. Sai ya ce "kada ka yi magana da su kuma kada ka karbi ruwaya daga wurinsu domin suna yin Karya”. - Minhajus Sunnatun Nabawiyya 1/26 NA BIYU: IMAM SHAFI'I Ruwaya ta inganta daga gare shi ya ce " A cikin 'yan bidi a kaf ban taba ganin wanda ya fi Rafilawa karyaba da shaidar Zur.” - Al-Inabatul Kubra 2/545 NA UKU: IMAM AHMAD An karbo daga Abdullah bin Ahmad ya ce: “ Na tambayi babana dangane da mutumin da yake zagi daya daga sahabban manzon Allah.” Sai yace " Bana ganin yana kan Musulumci”. - Kitabus Sunnah 1/493 Kuma harwayau an tambaye shi dangane da mutumin da yake da makwafci Dan Shi'ah: ...