Tarihin Sahabbai Mata 3: Ummu Adiyya Al-Ansariyya
UMMU ADIYYA
AL-ANSARIYYA
"Ta halacci yakoki bakwai tare
da Manzon Allah"
- Mausu’ at
Hayatis-sahabiyyat
Sunanta
Nusaiba bnt Haris (نسيبة بن حارث), a wata fadar kuma bnt Ka’ab (بنت كعب). Amma Abu Amr ya musunta hakan yace
Nusaiba bnt Ka’ab (نسيبة بنت كعب) ita ce Ummu Ammara (أم عمارة), amma ita wannan an fi
saninta da Ummu Adiyya (أم عادية الأنصارية).
-
Al-Isabah 8/437
Ibn
Sa’ad
yace "Ummu Adiyya ta musulunta tun da wuri kuma ta halacci yakoki da masu
yawa tare da manzon Allah. Kuma ta ruwaici hadisai masu yawa daga gareShi".
-
Dabakaat, 455
An
ruwaito daga wajenta tana cewa "Na halacci yakoki bakwai (7) tare da Manzon Allah ﷺ mun
kasance muna dafa musu abinci, kuma muna kula da abin hawansu tare da yin
magani ga wadanda aka yi wa rauni muna kuma jinyarsu"
-
Mausu at Hayatis sahabiyyat
Imamuz-Zahabiy
yace "Ummu Adiyya tana cikin mafiya sani cikin sahabbai ta ruwaito
hadisai masu yawa"
-
Siyaru 2/318
Lokacin
da 'yar Manzon Allah ﷺ ta rasu, wato Zainab Ummu Adiyya tana cikin wadanda suka
yi mata wanka kamar yadda Muhammad bin Sirina ya ruwaito daga gareta tana cewa:
"Manzon Allah ﷺ ya shiga wurinmu yayin da 'yarsa Zainab ta rasu
sai yace :
اغْسِلْنَهَا ثَلاَثًا أَوْ خَمْسًا أَوْ
أَكْثَرَ مَنْ ذَلِكَ إِنْ رَأَيْتُنَّ ذَلِكَ بِمَاءٍ وَسِدْرٍ، وَاجْعَلْنَ فِي
الآخِرَةِ كَافُورًا أَوْ شَيْئًا مِنْ كَافُورٍ، فَإِذَا فَرَغْتُنَّ فَآذِنَّنِي. فَلَمَّا فَرَغْنَا آذَنَّاهُ فَأَعْطَانَا حِقْوَهُ فَقَالَ " أَشْعِرْنَهَا إِيَّاهُ ". تَعْنِي إِزَارَهُ.
"ku wanke ta sau uku (3) ko sau biyar (5) ko fiye da haka idan kun so
da ruwa da magarya a karshen wankewar ku sanya kafur ko wani abu daga kafur
in dai kun gama ku gaya min" ta ce: "Ya yin da muka gama sai muka
gaya masa sai ya bamu mayafinsa" Yace "ku lullubeta da shi"
- Bukhari
1253, Muslim 939
An ce
Ummu Adiyya Mace ce mai yawan kyauta da
sadaka da taimakon raunana.
An
ce bayan wafatin Manzon Allah, Ummu Adiyya ta tashi daga madina ta koma Basra.
An ruwaito cewa khalifa Aliya Bin Abi Dalib har yakan yawan ziyararta a gidanta
har ya kwanata ya yi kailula a gidanta.
26th Muharram, 1439AH
(17th October, 2017CE)
Comments
Post a Comment