Tarihin Sahabbai Mata 2: Ummu Rumana

UMMU RUMANA AL-KINANIYAH
(أم رومان الكنانیة)




Sunanta Ummu Rumana bint Amir ibn Umaymir bn Abdulsham ibn Attab ibn Uzaifah ibn Subi'i bn Duhman ibn al-Haris ibn Ghanam ibn Malik ibn Kinana (رضي الله عنھا و أرضاھا). Ita ‘yace ga ‘Amir ibn Umaymir wanda su Banu Kinanahne. Sunan na asali shi ne Zainab kamar yadda aka ruwaito daga Ibn Ishaq.
- Al’isaba 8/391

Ummu Rumana ta kasance mata gun Khalifan Manzon Allah Abubakar as-Siddiq (R), kuma mahaifiya ga Nana A’isha da AbdurRahman bin Abubakar Assiddiq.  Ana mata kirari da cewa "Duk wanda yake son ya ga Hurul'ini tun a duniya to ya dubi Ummu Rumana".
- Tahzibul Kamal 35/259

A zamanin jahiliyya ta auri wani da ake kira Al-Haris bn Sakhbarah (الحارث بن سخبرة) ta Haifa masa al-Dufail. Bayan rasuwarsa sai ta auri Abubakar As-Siddiq (R). Ta musulunta tun da wuri ta mika wuya ga manzon Allah, sannan ta yi hijira zuwa Madina tare da Iyalan Gidan Manzon Allah da 'ya'yanta da dukkan iyalan Abubakar, Allah Ya kara musu yarda.
- At-Tabaqaat 8/276

Ummu Rumana ta kasance salaha, mutumiyar kirki abar kwatance.

Ummu Rumana ta rasu a zamanin Manzon Allah a watan Dhul-Hijja shekara ta shida (6) bayan Hijira a , an ce ya yin da ta rasu Manzon Allah ne ya shiga cikin kabarinta, sannan ya ce:
"من سره أن ينظر إلى امرة من الحور العين فلينظر إلى أم رومان"
“WANDA DUK YAKE SO YA GA HURUL-INI TUN A DUNIYA TO YA DUBI UMMU RUMANA”. Sannan Manzon Allah Ya nema mata gafara.
- Al-Isaba 8/391, Musnad 6/212, Ibn Hajar a Fathul-Bari 7/438; da Mausu'at Hayatis Sahabiyyat.

Ka’ab Saleh Abdulkarim
24th Muharram, 1439AH
15th October, 2017CE

Comments

Popular posts from this blog

Tarihin Sahabbai Mata 1: Maimunatu bint al-Harith (R)

Sahabbai 12 da aka fi ruwaito hadisan Annabi S.A.W. daga garesu

Tarihin Sahabbai 10: 1. Muaz bin Jabal (R)