Maganganun Malamai akan Mummunar Akidar Shia
MAGANGANUN MALAMAI AKAN MUMMUNAR AKIDAR SHI'AH
GA KADAN DAGA CIKI
NA FARKO: IMAM MALIK BN ANAS
An ruwaitu daga Imam Malik yace:
"Wanda yake zagin sahabban Manzon Allah bai da rabo ko kuma cewa ya
yi bai da kaso a cikin Musulunci"
Almajirin Imam Malik mai suna
Ashhabu ya ce: An tambayi malik dangane da Rafilawa”. Sai ya ce
"kada ka yi magana da su kuma kada ka karbi ruwaya daga wurinsu domin suna
yin Karya”.
- Minhajus Sunnatun Nabawiyya 1/26
NA BIYU: IMAM SHAFI'I
Ruwaya ta inganta daga gare shi ya
ce "A cikin 'yan bidi a kaf ban taba ganin wanda ya fi Rafilawa
karyaba da shaidar Zur.”
- Al-Inabatul Kubra 2/545
NA UKU: IMAM AHMAD
An karbo daga Abdullah bin Ahmad
ya ce: “Na tambayi babana dangane da mutumin da yake zagi daya daga sahabban
manzon Allah.” Sai yace "Bana ganin yana kan Musulumci”.
- Kitabus Sunnah 1/493
Kuma harwayau an tambaye shi
dangane da mutumin da yake da makwafci Dan Shi'ah: “Yana iya yi masa
sallama? Sai ya ce "A'a, sam kuma idan shi ya yi masa
sallama kada ya amsa."
- Kitabus Sunnah 1/494
NA HUDU: ALKALI IYAD ALMALIKIY
Wanda ya shahara da littafinsa
Ashafa ()
Yana cewa:"Haka nan kuma
muna yanke hukunci da kafircin gulatu Rafilawa wadanda suka ce Imamai sun fi
Annabawa falala”.
- Ashifa 2/1078
NA BIYAR: IMAM DAHAWI
Ya fadi acikin Akidarsa “kuma
muna son sahabban manzon Allah ba ma takaitawa wajen son dayansu, kuma ba ma
barranta daga dayansu, muna kin wanda yake kin su kuma yake ambaton su ba da
alheri ba mu ba ma ambaton su sai da alheri. Mun kudure cewa sonsu addini ne da
imani da ihsani kuma kinsu (kuma) kafirci ne da munafunci da zalunci”
- Al’akidatul Dahawiyya shafi na
689
NA SHIDA: IMAM AHMAD BIN ABDULHALIM
BIN ABDULSALAM BIN TAIMIYYA
Yana cewa :"Allah ya
sani kuma Allah ya isa masani cewa a cikin kungiyoyin bidi'ah duka masu
danganta kansu da musulunci babu wanda ya fi su sharri da jahilci da karya da
zulunci da sabo haka nan babu wanda ya fi su nisa da hakikanin imani wato
Rafilawa”.
- Minhajus sunnah 1/160
NA BAKWAI: MUJADDADI DANFODIYO
Shi ne wanda akan sa zandakata shi.
Shi shaihu Usman Danfodiyo a zamanin sa
babu su a kasar nan amma yana sane da su da miyagun akidojinsu bayan ya ruwaitu
maganar Hafiz ibn Hajar inda yake cewa: "wanda duk ya kafirta
sahabban ko ya ce al'umma ta bata to shi kafiri ne" sai ya
ce "Na ce haka nan duk wanda ya yi shakkar kafircinsa shi ma kafiri
ne."
Dubi yadda Shaihu Mujaddadi ya
kafirta mai shakkun kafircin Dan Shi'ah ta hakane za ka Fahimci cewa kafircin
'yan Shi'ah yana da kaushi ainun.
Allah Ka karemu daga wannan mummunar
akidar, amin.
✍ Mal. Ka'ab Saleh
24th Muharram, 1439AH
15th October, 2017CE
Comments
Post a Comment