Danduba da Boka
DANDUBA (ARRAF)
DA BOKA
1. DAN DUBA (ARRAF )
Mai Duba, shi ne wanda yake da’awa sanin abin da ya buya (sirri) ta
hanyar wasu abubuwa da suke gabata ya kafa dalili dasu a kan sanin abin da aka
sace da wajen da abin ya bace yake da makamancin haka.
2. BOKA
Boka kuwa, shi ne wanda yake bayar da labarin abin da zai zo nan
gaba. A wani fadin kuma aka ce: shi ne wanda yake da’awar sanin abin da ke
cikin zuciya ta hanyar sihiri da amfani da aljannu. (أحاديث السحر والرقية فى الكتب والسنة: 90).
Abul Abbas Ibn Taimiyya yace: Al-arraf suna ne na Boka da mai ilimin
taurari da mai duba (ta hanyar buga kasa) da makamancinsu, na wadanda suke
magana a kan sanin al’amura ta wadannan hanyoyi. Kuma Ibn Abbas yace dangane da
mutane masu ilimin hisabin haruffa kuma suke duba tafiyar taurari yace bana
ganin wanda ya aikata wannan yana da wani rabo a gurin Allah.
An karbo hadisi daga Abu Hurairah (RA), Manzon Allah (SAW):
"اجتنبوا السبع الموبقات" قالو: يا رسول الله وما من؟
قال: "الشرك بالله، والسحر، وقتل النفس التى حرم إلا بالحق، وأكل الربا، وأكل
مال اليتيم والتولي يوم الزحف، وقذف الحصنات المؤمنات الغافلات"
“Ku nesanci abubuwa masu halakarwa guda bakwai,
sai akace ya Manzon Allah mene ne su? Ya ce, Tarayya da Allah, da Sihiri (zuwa
gun boka, ko yin tsafi), da kisan kai wanda Allah Ya haramta, sai da gaskiya, da
cin dukiyar marayu, da cin Riba, da juya baya a fagen yaki (watau gudu), da karya
(kage) wa muminan mata tsararru (masu kamun kai) wadanda suka tsare kansu.
- Fathul Bari 3/62
MENENE HUKUNCIN WANDA YAJE WAJAN BOKA
Hadisi ya tabbata acikin Sahihu muslim.
Manzon Allah yace "Duk wanda ya Je gurin boka ya tambaye shi
wani abu kuma ya gaskata abin da ya ba shi labari to ba za a karbi sallarsa ta
kwana arba, in ba "
Da hadisin Abu Hurairah (R.A.) daga Manzon Allah yace:
" من أتى عرافا أو كاهنا فصدقه بما يقول فقد كفر بما أنزل على
محمد".
"Duk wanda ya je gurin boka kuma ya gaskata abin da yake fadi
to hakika ya kafircewa Abin da aka saukar wa manzon Allah "
- Targhib 4/53: Abu
Dauda, Ibn Majah, Tirmidhi da Hakim su
ne suka ruwaito
A wata ruwayar ma, ba za a karbi ibadar
mutum ba ta kwanaki arba’in (40), da
makamantan irin wannan hadisai wanda suke tsoratar damu zuwa wajan boka ko
danduba Allah kakara shiryar damu akan bin sunnar manzon ka kakara nesantamu
daga wadannan mutanen masu wannan halaye, Allah kabamu ikon bin gaskiya da kuma
aiki da ita.
خير الكلام من قل ودل، سبحانك اللهم وبحمدك،
أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك
22nd Muharamma, 1438AH
(10th October, 2017CE)
Comments
Post a Comment